HABBATUS-SAUDA (kashi na hudu)
HABBATUS-SAUDA ko muce HABBATUL-BARAKA duka sunayenta ne, takasance kwaya ce wacce take da albarka, tana maganin kowani irin cuta da yardan ALLAH.
Maganin 'kari dake fitowa kan fata.
Shi dai ciwon'kari, ciwo ne da ake kiransa da cutar kuturta, wanda mafi yawan al'umma ke kyamar wanda yakamu da ita, gani sukeyi kamar ba a warkewa diga cutar.
Alamomin cutar kuturta mutum zai ji:
1. Yawan kaikayin hannu ko kafa
2. Fitar ruwa kan hannun mutum ko kafa
3. Fitar kuraje a hannu ko kafa
4. Hannun ko kafar mutum yanemi tonkorewa
5. Wadannan sune manyan alamomin ciwon.
Yadda ake maganin ciwon'kari ko kuturta da HABBATUS-SAUDA za a samu:
1. Garin HABBATUS-SAUDA
2. Man HABBATUS-SAUDA
3. Man ZAITUN
Sai a hadasu waje guda acakuda su sosai, sai atafasa ruwa, yadafu sosai, sai abar ruwa ya huce, yadda zaizama da dumi, dumin da mutum zai iya amfani dashi be zai cutar ba.
Sai a debe wannan maganin da aka hada cokali uku asa a cikin ruwan, ruwan kar yawuce kimanin Kofi hudu zuwa shida.
Sai mutum yasa kafarsa ko hannun sa mai ciwon, har sawon lokacin da ruwan zafin zai huce. (Ba'a shan ruwan).
Za a ringa yin haka sau uku a rana, na sawon wata daya, Insha ALLAH za'a rabu da ciwon.
Muna godiya da ziyartar wannan shafi, ataimaka amana like da share don saura su amfana.
Comments
Post a Comment