Posts

Showing posts from February, 2021
Image
  HABBATUS-SAUDA (kashi na hudu) HABBATUS-SAUDA ko muce HABBATUL-BARAKA duka sunayenta ne, takasance kwaya ce wacce take da albarka, tana maganin kowani irin cuta da yardan ALLAH. Maganin 'kari dake fitowa kan fata. Shi dai ciwon'kari, ciwo ne da ake kiransa da cutar kuturta, wanda mafi yawan al'umma ke kyamar wanda yakamu da ita, gani sukeyi kamar ba a warkewa diga cutar. Alamomin cutar kuturta mutum zai ji: 1. Yawan kaikayin hannu ko kafa 2. Fitar ruwa kan hannun mutum ko kafa 3. Fitar kuraje a hannu ko kafa 4. Hannun ko kafar mutum yanemi tonkorewa 5. Wadannan sune manyan alamomin ciwon. Yadda ake maganin ciwon'kari ko kuturta da HABBATUS-SAUDA za a samu: 1. Garin HABBATUS-SAUDA 2. Man HABBATUS-SAUDA 3. Man ZAITUN Sai a hadasu waje guda acakuda su sosai, sai atafasa ruwa, yadafu sosai, sai abar ruwa ya huce, yadda zaizama da dumi, dumin da mutum zai iya amfani dashi be zai cutar ba. Sai a debe wannan maganin da aka hada cokali uku asa a cikin ruwan, ruwan kar yawu...
Image
  HABBATUS-SAUDA (kashi na uku ) HABBATUS-SAUDA kwaya ce mai albarka wacce ba'a qayyade iya maganin da takeyi ba, ita HABBATUS-SAUDA tana maganin kowani irin cuta, sai dai tanada hanyoyi daban-daban wajen sarrafata don yin magani. Yadda ake maganin AMOSANI da HABBATUS-SAUDA Ita dai cutar AMOSANI cuta ce wacce malaman kiwon lafiya sukace tana cikin jinin mutum, wanda take hana jinin mutum gudana yadda yadace, takan sa jinin mutum yazama ruwa-ruwa sai taje tataru acikin gefen kan mutum. Alamomin da suke nuna cewa mutum nada ciwon AMOSANI gasu kamar haka: 1. Mutum zai ringa jin idonsa akwai alamar 'kasa ko tsakuwa 2. Mutum zai rufe idonsa yaringa qaiqayawa kamar 'kasa tashiga ciki amma ba abinda yashiga ciki 3. Mutum zai ji yana yawan jin bacci kuma in yakwanta zaiyi baccin 4. Mutum zai ringa jin kasala 5. Idan mutum yafita a titi yana tafiya, sai yasa hannu yana kare idanun sa, bai son rana ta haska idon nasa, idan yabari rana ta haska idonsa zaiji zafi 6. Mutum zaiga idan y...
Image
  HABBATUS-SAUDA (kashi na biyu)  HABBATUS-SAUDA kwaya ce mai albarka wacce take maganin cututtuka daban-daban , hasalima ANNABI MUHAMMAD S.A.W. yace tana maganin kowani irin cuta sai dai MUTUWA. Diga cikin cututtukan da take magani akwai kamar haka: 1. Amosani ko Amodari 2. Qarin dake fitowa akan fata 3. Ciwon baya da ciwon kirji 4. Ciwon Mahaifa 5. Ciwon Mafitsara 6. Ciwon Hawan Jini 7. Ciwon Mura mai Zazzabi mai karfi 8. Ciwon Kai mai Tsanani 9. Maganin karyewar gashin kai na Mace 10. Ciwon Diabetes 11. Ciwon kwoda 12. Ciwon Taifot 13. Ciwon kunne 14. Ciwon Hakori 15. Shafan Aljanu ko sihiri 16. Matsalar Al'auran namiji ko Al'uran Mace Insha ALLAH wannan shafin zaiyi kokari yakawo muku bayani akan yadda za'ayi amfani da HABBATUS-SAUDA don magance wadannan cututtuka da muka lissafo. Mungode da ziyartar wannan shafin Magani cikin Abinci , kar amanta adanna mana  like na page namu da wannan posting da mukayi sa'annan adanna mana  share don sauran'yan uwa su am...
Image
  HABBATUS-SAUDA (Kashi na daya) HABBATUS-SAUDA wata kwaya ce wacce take da albarka, wacce ANNABI MUHAMMAD S.A.W. Ya ambace ta, Imamul Bukhari yafitar da hadisi acikin littafi mai suna KITABUL-TIB yasama babin suna, BABUN HABBATUS-SAUDA. Ita wannan kwaya ana kiranta da sunaye kamar haka: HABBATUS-SAUDA HABBATUL-BARAKA SAUDA'UL-KAMUN KAMUNAL-ASWAD Akwai Hadisai guda biyu, gameda wannan kwaya mai labarka (HABBATUL-BARAKA). (1) An ruwaito diga NANA-AISHA ALLAH yakara mata yarda, tace naji MANZON ALLAH S.A.W. yace " acikin wannan HABBATUS-SAUDA tana maganin dukkan cututtuka sai dai cutar SAM ". Sai nace ya RASULULLAH menene SAM? Sai yace min MUTUWA. (2) An ruwaito diga Abu-Huraira yace naji MANZON ALLAH S.A.W. Yace " Acikin HABBATUS-SAUDA maganine ta kowani irin cuta sai dai SAM (MUTUWA) ". Mungode da samun lokacin wajen ziyartar wannan sahafi, ataimaka ayi share don sauran yan uwa su amfana, kuma Kai/ke za'a samu lada.